Surah Al-Fil (The Elephant)

Listen

Hausa

Surah Al-Fil (The Elephant) - Aya count 5

أَلَمۡ تَرَ كَیۡفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِأَصۡحَـٰبِ ٱلۡفِیلِ ﴿١﴾

Ashe, ba ka ga yadda Ubangijin ka Ya aikata ga mutanen giwa* ba?

* An yi Yãƙin Gĩwa shekarar haihuwar Annabi tsakãnin halaka su da haihuwarsa kwãna hamsin. Bayan shekara arba'in Annabi ya fara karantar da mutane. Ya karantar da su cikin shekara ashirin da uku, sa'an nan ya ƙaura. Bayansa da shekara hamsin waanda suka bi shi suka cinye duniya. Wannan yana nuna cewa mutane ba su samun daraja sai da riƙon addini da ilimi.


Arabic explanations of the Qur’an:

أَلَمۡ یَجۡعَلۡ كَیۡدَهُمۡ فِی تَضۡلِیلࣲ ﴿٢﴾

Ashe, bai sanya kaidin su a cikin ɓata ba?


Arabic explanations of the Qur’an:

وَأَرۡسَلَ عَلَیۡهِمۡ طَیۡرًا أَبَابِیلَ ﴿٣﴾

Kuma Ya sako, a kansu, wasu tsuntsãye, jama'a-jama'a.


Arabic explanations of the Qur’an:

تَرۡمِیهِم بِحِجَارَةࣲ مِّن سِجِّیلࣲ ﴿٤﴾

Suna jifar su da wasu duwatsu na yumɓun wuta.


Arabic explanations of the Qur’an:

فَجَعَلَهُمۡ كَعَصۡفࣲ مَّأۡكُولِۭ ﴿٥﴾

Sa'an nan Ya sanya su kamar karmami wanda aka cinye?


Arabic explanations of the Qur’an: