Surah An-Nazi'at (Those who Pull Out)

Listen

Hausa

Surah An-Nazi'at (Those who Pull Out) - Aya count 46

وَٱلنَّـٰزِعَـٰتِ غَرۡقࣰا ﴿١﴾

Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَٱلنَّـٰشِطَـٰتِ نَشۡطࣰا ﴿٢﴾

Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَٱلسَّـٰبِحَـٰتِ سَبۡحࣰا ﴿٣﴾

Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.


Arabic explanations of the Qur’an:

فَٱلسَّـٰبِقَـٰتِ سَبۡقࣰا ﴿٤﴾

Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umarnin Allah) kamar suna tsẽre.


Arabic explanations of the Qur’an:

فَٱلۡمُدَبِّرَ ٰ⁠تِ أَمۡرࣰا ﴿٥﴾

Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umarni.


Arabic explanations of the Qur’an:

یَوۡمَ تَرۡجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ ﴿٦﴾

Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.


Arabic explanations of the Qur’an:

تَتۡبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ ﴿٧﴾

Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.


Arabic explanations of the Qur’an:

قُلُوبࣱ یَوۡمَىِٕذࣲ وَاجِفَةٌ ﴿٨﴾

Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.


Arabic explanations of the Qur’an:

أَبۡصَـٰرُهَا خَـٰشِعَةࣱ ﴿٩﴾

Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.


Arabic explanations of the Qur’an:

یَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرۡدُودُونَ فِی ٱلۡحَافِرَةِ ﴿١٠﴾

Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?


Arabic explanations of the Qur’an:

أَءِذَا كُنَّا عِظَـٰمࣰا نَّخِرَةࣰ ﴿١١﴾

"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"


Arabic explanations of the Qur’an:

قَالُواْ تِلۡكَ إِذࣰا كَرَّةٌ خَاسِرَةࣱ ﴿١٢﴾

Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"


Arabic explanations of the Qur’an:

فَإِنَّمَا هِیَ زَجۡرَةࣱ وَ ٰ⁠حِدَةࣱ ﴿١٣﴾

To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.


Arabic explanations of the Qur’an:

فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ ﴿١٤﴾

Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.


Arabic explanations of the Qur’an:

هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِیثُ مُوسَىٰۤ ﴿١٥﴾

Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?


Arabic explanations of the Qur’an:

إِذۡ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلۡوَادِ ٱلۡمُقَدَّسِ طُوًى ﴿١٦﴾

A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?


Arabic explanations of the Qur’an:

ٱذۡهَبۡ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ ﴿١٧﴾

Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.


Arabic explanations of the Qur’an:

فَقُلۡ هَل لَّكَ إِلَىٰۤ أَن تَزَكَّىٰ ﴿١٨﴾

"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَأَهۡدِیَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخۡشَىٰ ﴿١٩﴾

"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoron Sa?"


Arabic explanations of the Qur’an:

فَأَرَىٰهُ ٱلۡـَٔایَةَ ٱلۡكُبۡرَىٰ ﴿٢٠﴾

Sai ya nũna masa ãyar* nan mafi girma.

* Ãyar Mũsã da ta fi girma ita ce sandarsa mai zama maciji ko hannunsa mai haske kamar tõcila idan yã sanya cikin hammata yã fitar.


Arabic explanations of the Qur’an:

فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ ﴿٢١﴾

Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),


Arabic explanations of the Qur’an:

ثُمَّ أَدۡبَرَ یَسۡعَىٰ ﴿٢٢﴾

Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.


Arabic explanations of the Qur’an:

فَحَشَرَ فَنَادَىٰ ﴿٢٣﴾

Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.


Arabic explanations of the Qur’an:

فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلۡأَعۡلَىٰ ﴿٢٤﴾

Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."


Arabic explanations of the Qur’an:

فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلۡـَٔاخِرَةِ وَٱلۡأُولَىٰۤ ﴿٢٥﴾

Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.


Arabic explanations of the Qur’an:

إِنَّ فِی ذَ ٰ⁠لِكَ لَعِبۡرَةࣰ لِّمَن یَخۡشَىٰۤ ﴿٢٦﴾

Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.


Arabic explanations of the Qur’an:

ءَأَنتُمۡ أَشَدُّ خَلۡقًا أَمِ ٱلسَّمَاۤءُۚ بَنَىٰهَا ﴿٢٧﴾

Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.


Arabic explanations of the Qur’an:

رَفَعَ سَمۡكَهَا فَسَوَّىٰهَا ﴿٢٨﴾

Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَأَغۡطَشَ لَیۡلَهَا وَأَخۡرَجَ ضُحَىٰهَا ﴿٢٩﴾

Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ ذَ ٰ⁠لِكَ دَحَىٰهَاۤ ﴿٣٠﴾

Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.


Arabic explanations of the Qur’an:

أَخۡرَجَ مِنۡهَا مَاۤءَهَا وَمَرۡعَىٰهَا ﴿٣١﴾

Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَٱلۡجِبَالَ أَرۡسَىٰهَا ﴿٣٢﴾

Da duwatsu, Yã kafe ta.


Arabic explanations of the Qur’an:

مَتَـٰعࣰا لَّكُمۡ وَلِأَنۡعَـٰمِكُمۡ ﴿٣٣﴾

Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.


Arabic explanations of the Qur’an:

فَإِذَا جَاۤءَتِ ٱلطَّاۤمَّةُ ٱلۡكُبۡرَىٰ ﴿٣٤﴾

To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.


Arabic explanations of the Qur’an:

یَوۡمَ یَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَـٰنُ مَا سَعَىٰ ﴿٣٥﴾

Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَبُرِّزَتِ ٱلۡجَحِیمُ لِمَن یَرَىٰ ﴿٣٦﴾

Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.


Arabic explanations of the Qur’an:

فَأَمَّا مَن طَغَىٰ ﴿٣٧﴾

To, amma wanda ya yi girman kai.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَءَاثَرَ ٱلۡحَیَوٰةَ ٱلدُّنۡیَا ﴿٣٨﴾

Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).


Arabic explanations of the Qur’an:

فَإِنَّ ٱلۡجَحِیمَ هِیَ ٱلۡمَأۡوَىٰ ﴿٣٩﴾

To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَأَمَّا مَنۡ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفۡسَ عَنِ ٱلۡهَوَىٰ ﴿٤٠﴾

Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.


Arabic explanations of the Qur’an:

فَإِنَّ ٱلۡجَنَّةَ هِیَ ٱلۡمَأۡوَىٰ ﴿٤١﴾

To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.


Arabic explanations of the Qur’an:

یَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَیَّانَ مُرۡسَىٰهَا ﴿٤٢﴾

Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?


Arabic explanations of the Qur’an:

فِیمَ أَنتَ مِن ذِكۡرَىٰهَاۤ ﴿٤٣﴾

Me ya haɗã ka da ambatonta?


Arabic explanations of the Qur’an:

إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَاۤ ﴿٤٤﴾

Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.


Arabic explanations of the Qur’an:

إِنَّمَاۤ أَنتَ مُنذِرُ مَن یَخۡشَىٰهَا ﴿٤٥﴾

Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.


Arabic explanations of the Qur’an:

كَأَنَّهُمۡ یَوۡمَ یَرَوۡنَهَا لَمۡ یَلۡبَثُوۤاْ إِلَّا عَشِیَّةً أَوۡ ضُحَىٰهَا ﴿٤٦﴾

Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.


Arabic explanations of the Qur’an: