Surah At-Takwir (The Overthrowing)

Listen

Hausa

Surah At-Takwir (The Overthrowing) - Aya count 29

إِذَا ٱلشَّمۡسُ كُوِّرَتۡ ﴿١﴾

Idan rãna aka shafe haskenta


Arabic explanations of the Qur’an:

وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتۡ ﴿٢﴾

Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).


Arabic explanations of the Qur’an:

وَإِذَا ٱلۡجِبَالُ سُیِّرَتۡ ﴿٣﴾

Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَإِذَا ٱلۡعِشَارُ عُطِّلَتۡ ﴿٤﴾

Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna* aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.

* Rãƙuma mãsu ciki ɗan wata gõma.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَإِذَا ٱلۡوُحُوشُ حُشِرَتۡ ﴿٥﴾

Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَإِذَا ٱلۡبِحَارُ سُجِّرَتۡ ﴿٦﴾

Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتۡ ﴿٧﴾

Kuma idan rãyuka aka haɗa* su da jikunkunansu.

* Ko kuma, aka haɗa kõwane mutum da irin mutãnensa a Aljanna ko a wuta.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَإِذَا ٱلۡمَوۡءُۥدَةُ سُىِٕلَتۡ ﴿٨﴾

Kuma idan wadda aka turbuɗe* ta da rai aka tambaye ta.

* A cikin zãmanin jahiliyya Lãrabãwa bã su son a haifa musu 'ya'ya mãta dõmin haka har sukan turbuɗe 'ya'yansu dõmin kada su yi abin kunya ko kuma su talauce wajen yi musu aure.


Arabic explanations of the Qur’an:

بِأَیِّ ذَنۢبࣲ قُتِلَتۡ ﴿٩﴾

"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"


Arabic explanations of the Qur’an:

وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتۡ ﴿١٠﴾

Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).


Arabic explanations of the Qur’an:

وَإِذَا ٱلسَّمَاۤءُ كُشِطَتۡ ﴿١١﴾

Kuma idan sama aka fẽɗe ta.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَإِذَا ٱلۡجَحِیمُ سُعِّرَتۡ ﴿١٢﴾

Kuma idan Jahĩm aka hũra ta


Arabic explanations of the Qur’an:

وَإِذَا ٱلۡجَنَّةُ أُزۡلِفَتۡ ﴿١٣﴾

Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.


Arabic explanations of the Qur’an:

عَلِمَتۡ نَفۡسࣱ مَّاۤ أَحۡضَرَتۡ ﴿١٤﴾

Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).


Arabic explanations of the Qur’an:

فَلَاۤ أُقۡسِمُ بِٱلۡخُنَّسِ ﴿١٥﴾

To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã* ba.

* Masu tafiya suna kõmawa bãya.


Arabic explanations of the Qur’an:

ٱلۡجَوَارِ ٱلۡكُنَّسِ ﴿١٦﴾

Mãsu gudu suna ɓũya.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَٱلَّیۡلِ إِذَا عَسۡعَسَ ﴿١٧﴾

Da dare idan ya bãyar da bãya.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَٱلصُّبۡحِ إِذَا تَنَفَّسَ ﴿١٨﴾

Da sãfiya idan ta yi lumfashi.


Arabic explanations of the Qur’an:

إِنَّهُۥ لَقَوۡلُ رَسُولࣲ كَرِیمࣲ ﴿١٩﴾

Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.


Arabic explanations of the Qur’an:

ذِی قُوَّةٍ عِندَ ذِی ٱلۡعَرۡشِ مَكِینࣲ ﴿٢٠﴾

Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.


Arabic explanations of the Qur’an:

مُّطَاعࣲ ثَمَّ أَمِینࣲ ﴿٢١﴾

Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجۡنُونࣲ ﴿٢٢﴾

Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَلَقَدۡ رَءَاهُ بِٱلۡأُفُقِ ٱلۡمُبِینِ ﴿٢٣﴾

Kuma lalle ne, yã gan shi* a cikin sararin sama mabayyani.

* Annabi ya ga Mala'ika Jibirilu ya san shi. Sabõda haka wani aljani bã zai yi kama da shi ba balle ya kãwo masa ƙarya.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَمَا هُوَ عَلَى ٱلۡغَیۡبِ بِضَنِینࣲ ﴿٢٤﴾

Kuma shi, ga gaibi* bã mai rowa ba ne.

* Ma'anar gaibi a nan, ilmin da Allah Ya aiko Jibirilu da shi zuwa ga Annabi Annabi ba ya ɓõye shi daga mutãne. Ga wata ƙira'a, wanda ake tuhuma, wãto ba a tuhumar Annabi, ga gaibin da ya faɗi cewa daga Allah yake, wato Alƙur'ãni duka gaskiya ne.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَمَا هُوَ بِقَوۡلِ شَیۡطَـٰنࣲ رَّجِیمࣲ ﴿٢٥﴾

Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.


Arabic explanations of the Qur’an:

فَأَیۡنَ تَذۡهَبُونَ ﴿٢٦﴾

Shin, a inã zã ku tafi?


Arabic explanations of the Qur’an:

إِنۡ هُوَ إِلَّا ذِكۡرࣱ لِّلۡعَـٰلَمِینَ ﴿٢٧﴾

Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.


Arabic explanations of the Qur’an:

لِمَن شَاۤءَ مِنكُمۡ أَن یَسۡتَقِیمَ ﴿٢٨﴾

Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَمَا تَشَاۤءُونَ إِلَّاۤ أَن یَشَاۤءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلۡعَـٰلَمِینَ ﴿٢٩﴾

Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.


Arabic explanations of the Qur’an: