Surah Al-Balad (The City)

Listen

Hausa

Surah Al-Balad (The City) - Aya count 20

لَاۤ أُقۡسِمُ بِهَـٰذَا ٱلۡبَلَدِ ﴿١﴾

Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari* ba.

* Allah Ya ce ba sai Ya yi rantsuwa da Makka ba, sa'an nan zã a san darajarta a lõkacinda Annabi yake a cikinta, kuma shi yana da haƙƙin zama a cikinta mahaifansa da zurriyarsa duka, ko da yake zai yi hijira sabõda fitinar kãfirai mãsu halaka dũkiyarsu kan adãwa da shi. Dã sun yi amfãni da dukiyar ga ayyukan alheri, dã yã fi musu.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَأَنتَ حِلُّۢ بِهَـٰذَا ٱلۡبَلَدِ ﴿٢﴾

Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَوَالِدࣲ وَمَا وَلَدَ ﴿٣﴾

Da mahaifi da abin da ya haifa.


Arabic explanations of the Qur’an:

لَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَـٰنَ فِی كَبَدٍ ﴿٤﴾

Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.


Arabic explanations of the Qur’an:

أَیَحۡسَبُ أَن لَّن یَقۡدِرَ عَلَیۡهِ أَحَدࣱ ﴿٥﴾

Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?


Arabic explanations of the Qur’an:

یَقُولُ أَهۡلَكۡتُ مَالࣰا لُّبَدًا ﴿٦﴾

Yana cẽwa "Na* halakarda dũkiya mai yawa,"

* Nã halaka dukiya mai yawa dõmin faɗã da addĩni.


Arabic explanations of the Qur’an:

أَیَحۡسَبُ أَن لَّمۡ یَرَهُۥۤ أَحَدٌ ﴿٧﴾

Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?


Arabic explanations of the Qur’an:

أَلَمۡ نَجۡعَل لَّهُۥ عَیۡنَیۡنِ ﴿٨﴾

Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?


Arabic explanations of the Qur’an:

وَلِسَانࣰا وَشَفَتَیۡنِ ﴿٩﴾

Da harshe, da leɓɓa biyu.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَهَدَیۡنَـٰهُ ٱلنَّجۡدَیۡنِ ﴿١٠﴾

Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi* biyu ba?

* Hanyar alheri da ta sharri.


Arabic explanations of the Qur’an:

فَلَا ٱقۡتَحَمَ ٱلۡعَقَبَةَ ﴿١١﴾

To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?


Arabic explanations of the Qur’an:

وَمَاۤ أَدۡرَىٰكَ مَا ٱلۡعَقَبَةُ ﴿١٢﴾

Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?


Arabic explanations of the Qur’an:

فَكُّ رَقَبَةٍ ﴿١٣﴾

Ita ce fansar wuyan bãwa.


Arabic explanations of the Qur’an:

أَوۡ إِطۡعَـٰمࣱ فِی یَوۡمࣲ ذِی مَسۡغَبَةࣲ ﴿١٤﴾

Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.


Arabic explanations of the Qur’an:

یَتِیمࣰا ذَا مَقۡرَبَةٍ ﴿١٥﴾

Ga marãya ma'abũcin zumunta.


Arabic explanations of the Qur’an:

أَوۡ مِسۡكِینࣰا ذَا مَتۡرَبَةࣲ ﴿١٦﴾

Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.


Arabic explanations of the Qur’an:

ثُمَّ كَانَ مِنَ ٱلَّذِینَ ءَامَنُواْ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلصَّبۡرِ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلۡمَرۡحَمَةِ ﴿١٧﴾

Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.


Arabic explanations of the Qur’an:

أُوْلَـٰۤىِٕكَ أَصۡحَـٰبُ ٱلۡمَیۡمَنَةِ ﴿١٨﴾

Waɗannan ne ma'abũta albarka*

* Ko kuwa waɗanda ake bai wa takardunsu da dãma, a Lãhira.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَٱلَّذِینَ كَفَرُواْ بِـَٔایَـٰتِنَا هُمۡ أَصۡحَـٰبُ ٱلۡمَشۡـَٔمَةِ ﴿١٩﴾

Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyin Mu, sũ ne ma'abũta shu'umci*

* Ko kuwa waɗanda ake bai wa takardunsu da hagu, a Lãhira.


Arabic explanations of the Qur’an:

عَلَیۡهِمۡ نَارࣱ مُّؤۡصَدَةُۢ ﴿٢٠﴾

A kansu akwai wata wuta abar kullewa.


Arabic explanations of the Qur’an: