Surah At-Tin (The Fig)

Listen

Hausa

Surah At-Tin (The Fig) - Aya count 8

بِّسۡمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحۡمَـٰنِ ٱلرَّحِیمِ وَٱلتِّینِ وَٱلزَّیۡتُونِ ﴿١﴾

Inã rantsuwa da Attinu da Azzaitũn.*

* Ibn Abbas ya ce: 'Attinu shi ne masallacin Nuhu a kan Judiyyi, Azzaitun Masallacin Baitil Muƙaddas.'.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَطُورِ سِینِینَ ﴿٢﴾

Da Dũr Sĩnĩna.*

* Dutsen da Allah Ya yi magana da Musa a kansa. Ma'anarsa dutse mai albarka sabõda itacen da ke kansa.


Arabic explanations of the Qur’an:

وَهَـٰذَا ٱلۡبَلَدِ ٱلۡأَمِینِ ﴿٣﴾

Da wannan gari* amintacce.

* Gari amintacce shi ne Makkah.


Arabic explanations of the Qur’an:

لَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَـٰنَ فِیۤ أَحۡسَنِ تَقۡوِیمࣲ ﴿٤﴾

Lalle ne, Mun halitta mutum a cikin mafi kyawon tsayuwa.


Arabic explanations of the Qur’an:

ثُمَّ رَدَدۡنَـٰهُ أَسۡفَلَ سَـٰفِلِینَ ﴿٥﴾

Sa'an nan, Muka mayar da shi mafi ƙasƙantar masu rauni


Arabic explanations of the Qur’an:

إِلَّا ٱلَّذِینَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ فَلَهُمۡ أَجۡرٌ غَیۡرُ مَمۡنُونࣲ ﴿٦﴾

Face waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, saboda haka suna da sakamako wanda bã ya yankewa.


Arabic explanations of the Qur’an:

فَمَا یُكَذِّبُكَ بَعۡدُ بِٱلدِّینِ ﴿٧﴾

To, bãyan haka mẽ ya sanya ka ka ƙaryata sakamako (wanda za a yi a bãyan Tãshin ¡iyãma)?


Arabic explanations of the Qur’an:

أَلَیۡسَ ٱللَّهُ بِأَحۡكَمِ ٱلۡحَـٰكِمِینَ ﴿٨﴾

Ashe Allah bã Shi ne Mafi mãsu hukunci kyãwon hukunci ba?*

* Ana son wanda ya karanta sũrar har ƙarshe ya ce بلى ,wato na'am, Allah Ya fi kowa kyãwon hukunci.


Arabic explanations of the Qur’an: