Surah Al-'alaq (The Clot)

Listen

Hausa

Surah Al-'alaq (The Clot) - Aya count 19

ٱقۡرَأۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلَّذِی خَلَقَ ﴿١﴾

Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.


Arabic explanations of the Qur’an:

خَلَقَ ٱلۡإِنسَـٰنَ مِنۡ عَلَقٍ ﴿٢﴾

Ya hahitta mutum daga gudan jini.


Arabic explanations of the Qur’an:

ٱقۡرَأۡ وَرَبُّكَ ٱلۡأَكۡرَمُ ﴿٣﴾

Ka yi karatu, kuma Ubangijinka shi ne Mafi karimci.


Arabic explanations of the Qur’an:

ٱلَّذِی عَلَّمَ بِٱلۡقَلَمِ ﴿٤﴾

Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami.


Arabic explanations of the Qur’an:

عَلَّمَ ٱلۡإِنسَـٰنَ مَا لَمۡ یَعۡلَمۡ ﴿٥﴾

Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.


Arabic explanations of the Qur’an:

كَلَّاۤ إِنَّ ٱلۡإِنسَـٰنَ لَیَطۡغَىٰۤ ﴿٦﴾

A'aha! Lalle, ne mutum haƙĩƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu).


Arabic explanations of the Qur’an:

أَن رَّءَاهُ ٱسۡتَغۡنَىٰۤ ﴿٧﴾

Dõmin yã ga kansa, yã wadãta.


Arabic explanations of the Qur’an:

إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلرُّجۡعَىٰۤ ﴿٨﴾

Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take.


Arabic explanations of the Qur’an:

أَرَءَیۡتَ ٱلَّذِی یَنۡهَىٰ ﴿٩﴾

Shin, kã ga wanda ke hana.


Arabic explanations of the Qur’an:

عَبۡدًا إِذَا صَلَّىٰۤ ﴿١٠﴾

Bãwã idan yã yi salla?


Arabic explanations of the Qur’an:

أَرَءَیۡتَ إِن كَانَ عَلَى ٱلۡهُدَىٰۤ ﴿١١﴾

Ashe, kã gani, idan (shi bãwan) ya kasance a kan shiriya?


Arabic explanations of the Qur’an:

أَوۡ أَمَرَ بِٱلتَّقۡوَىٰۤ ﴿١٢﴾

Ko ya yi umurni da taƙawa?


Arabic explanations of the Qur’an:

أَرَءَیۡتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰۤ ﴿١٣﴾

Ashe, kã gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya?


Arabic explanations of the Qur’an:

أَلَمۡ یَعۡلَم بِأَنَّ ٱللَّهَ یَرَىٰ ﴿١٤﴾

Ashe, bai sani ba cewa Allah Yanã gani?


Arabic explanations of the Qur’an:

كَلَّا لَىِٕن لَّمۡ یَنتَهِ لَنَسۡفَعَۢا بِٱلنَّاصِیَةِ ﴿١٥﴾

A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne zã Mu ja gãshin makwarkwaɗa.


Arabic explanations of the Qur’an:

نَاصِیَةࣲ كَـٰذِبَةٍ خَاطِئَةࣲ ﴿١٦﴾

Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi.


Arabic explanations of the Qur’an:

فَلۡیَدۡعُ نَادِیَهُۥ ﴿١٧﴾

Sai ya kirayi ƙungiyarsa.


Arabic explanations of the Qur’an:

سَنَدۡعُ ٱلزَّبَانِیَةَ ﴿١٨﴾

Zã Mu kirayi zabaniyãwa (mala'iku mãsu girma).


Arabic explanations of the Qur’an:

كَلَّا لَا تُطِعۡهُ وَٱسۡجُدۡ وَٱقۡتَرِب ۩ ﴿١٩﴾

A'aha kada ka bĩ shi. Kuma ka yi tawali'u,* kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka).

* Wato salla da sauran ibãdu.


Arabic explanations of the Qur’an: